Afirka ke nan
Wani dan kasar Sin mai shekaru 26 da haihuwa ya kewaya kasashe 10 na Afirka a kan keke a shekara daya, inda ya shafi kilomita dubu 16, yana kallon hakikanin Afirka da yake tunani da idanunsa
"A watan Satumba na shekarar 2016, na isa kasar Benin dake yammacin Afirka a kan keke daga kasar Sin, na kuma karade kasashe 10 na Afirka a cikin shekara daya. A kan hanyata, na gamu da abubuwa da dama masu ban sha'awa." Kalaman Yuan Jianglei a cikin bayaninsa mai taken "Wannan Ita Ce Afirka".
Takaitaccen bayaninsa
Yuan Jianglei, ma'aikacin wani kamfani ne na birnin Guangzhou na kasar Sin.
Ya taba koyar da Sinanci a kwalejin Confucius na jami'ar Abomey-Calavi ta kasar Benin daga shekarar 2014 zuwa 2016.
A watan Satumba na shekarar 2016, ya tashi daga nahiyar Afirka, inda ya kawaya kasashe 10 dake yammaci da arewacin Afirka da kuma kasashe 6 na nahiyar Asiya ciki har da kasar Turkiya. Ya shafe kimanin kilomita 15961 a wadannan tafiye-tafiye, kana ya dawo kasar Sin a watan Satumba na shekarar 2017.