in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron FOCAC: Sin za ta gabatar da sabbin matakan hadin gwiwa da kasashen Afirka
2018-08-28 19:31:38 cri
Qian Keming, mataimakin ministan kasuwancin kasar Sin, ya bayyana a yau Talata cewa, a yayin taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da za a kaddamar mako mai zuwa, kasar Sin za ta gabatar da wasu sabbin matakai na habaka hadin gwiwa da kasashen Afirka, inda za a dora muhimmanci kan yunkurin taimakawa kasashen Afirka samun damar raya kansu.

Jami'in ya kara da cewa, sabbin matakan da za a dauka za a hade su da shawarar "Ziri daya da Hanya daya", da ajandar raya nahiyar Afirka nan da shekarar 2063 da kungiyar tarayyar Afirka AU ta gabatar, da ajandar samun ci gaba mai dorewa nan da shekarar 2030 ta MDD, gami da tsare-tsaren raya kasa na kasashe daban daban dake nahiyar Afirka. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China