in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Burkina Faso na fatan nasarorin kasar Sin za su jagoranci Afirka wajen samun ci gaba
2018-08-27 11:24:53 cri
Gabannin taron koli na dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka ko kuma FOCAC a takaice,wanda za'a yi a watan gobe a birnin Beijing, shugaban kasar Burkina Faso, Roch Marc Christian Kaboré, ya zanta da 'yan jaridun kasar Sin, inda ya ce, kasar Sin ta samu bunkasuwar da ta kai ta ga zama kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya ne sakamakon himma da kwazon da jama'arta suka nuna gami da jagoranci nagari da shugabannin kasar suka yi, don haka yana fatan nasarorin da kasar Sin ta samu za su taimakawa kasashen Afirka wajen samun ci gaba.

Shugaba Kaboré ya ce, kasashen Afirka suna fatan yin koyi da kasar Sin, musamman ma a fannonin da suka jibanci habaka tattalin arzikin kasa da kyautata zaman rayuwar al'umma.

A cewar Kaboré, ziyararsa kasar Sin a wannan karo za ta karfafa hadin-gwiwa tsakanin Burkina Faso da kasar Sin, gami da hadin-gwiwa tsakanin yammacin Afirka da kasar Sin. Ya kuma yaba sosai da shawarar "ziri daya da hanya daya", abun da ya ce za ta iya inganta mu'amalar cinikayya tsakanin kasashe daban-daban da samar da wadata a duniya baki daya. Ya jaddada cewa, ra'ayin raya makomar bil'adama ta bai daya da shugaban kasar Sin ya fitar ita ma na da babbar ma'ana, wadda ya ce za ta iya fadada hadin-gwiwa da bunkasuwa tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China