in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya yi tsokaci kan yanayin da ake ciki a zirin Koriya
2018-08-26 16:41:22 cri
Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya furta a jiya Asabar cewa, matsayin da kasar Sin ta dauka dangane da batun nukiliya a zirin Koriya mai dorewa ne, kuma kasar ta bayyana shi a fili. Sa'an nan kasar ta Sin za ta ci gaba da musayar ra'ayi da bangarori masu ruwa da tsaki, don taimakawa wajen kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya, gami da tabbatar da kwanciyar hankali a arewa maso gabashin Asiya.

Kakakin ya fadi haka ne yayin da yake amsa tambayar da wani dan jarida ya yi masa, inda aka yi tambaya cewa, kasar Amurka ta ce, wai kasar Sin ta canza ra'ayinta dangane da batun nukiliya na zirin Koriya, lamarin da ya yi tasiri kan yunkurin kasashen Amurka da Koriya ta Arewa na daidaita batun nukiliya ta hanyar shawarwari, dangane da maganar, mene ne ra'ayin kasar Sin?

Game da wannan tambaya, kakakin kasar Sin ya amsa cewa, zancen bangaren Amurka ya saba da hakikanin yanayin da ake ciki, wanda ya nuna kasar ba ta kula da sauran kasashe ba. Zancen ya sa kasar Sin ta nuna damuwa sosai, kuma ta riga ta nuna rashin jin dadi ga kasar Amurka.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China