Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi tir da kisan jami'in wanzar da zaman lafiya a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya wato CAR.
An zargin mayakan kungiyar 'yan tawaye na Anti-Balaka da kashe sojan 'dan kasar Burundi dake aikin wanzar da zaman lafiya a kasar.
Sanarwar da kakakinsa Stephane Dujarric ya fitar, ta ruwaito Antonio Guterres na jajantawa iyalan marigayin da kuma gwamnatin kasar Burundi.
Sakatare Janar din ya kara da cewa, hari kan jami'an majalisar masu aikin wanzar da zaman lafiya ka iya zama laifin yaki da kan janyo sanyawa masu hannu takunkumi. (Fa'iza Mustapha)