Wakiliyar musamman ta shugaban kasar Sin Xi Jinping, kana mataimakiyar shugaban majalissar ba da shawara kan harkokin siyasa ta Sin a taro na 13 uwargida Su Hui, za ta halarci bikin rantsuwar zababben shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, taron da zai gudana gobe Lahadi a Harare fadar mulkin kasar.
Shugaba Mnangagwa ne dai ya gayyaci kasar Sin zuwa bikin rantsuwar ta sa, kamar yadda kakakin ma'aikatar wajen Sin Lu Kang ya sanar da hakan a Asabar din nan.(Saminu)