in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren ITU: akwai kyakkyawar makoma dangane da hadin kai tsakanin Sin da Afirka a fannin sadarwa
2018-08-22 16:36:47 cri
Babban sakataren gamayyar kungiyar sadarwa ta duniya (ITU) Zhao Houlin ya ce, Sin da kasashen Afirka na da babbar damar hada kai a fannin sadarwa, domin suna da makoma mai kyau a fannin, kuma ko shakka babu, hadin kai tsakanin bangarorin biyu zai kai wani sabon matsayi.

Zhao ya bayyana haka ne yayin zantawarsa da manema labarun kamfanin dillancin labaru na Xinhua, inda ya ce, wasu kasashen Afirka da dama na fatan cimma burinsu na dogara da kansu wajen tabbatar da samun ci gaban tattalin arzikin nahiyar Afirka, kana suna fatan matsakaita da kanana kamfanoni za su taka muhimmiyar rawa a fannin, musamman ma ta fuskar rayawa da amfani da manyan kayayyakin more rayuwa na sadarwa. Kasar Sin ta samu fasahohi da dama wajen amfani da fasahar sadarwa da matsakaici da kanana kamfanoni ke yi, hakan zai amfana wa hadin kai a tsakanin bangarorin Sin da Afirka.

Ban da wannan kuma, Zhao ya ce, hadin kai tsakanin Sin da Afrika ya samu ci gaba a 'yan shekarun da suka gabata. Taron kolin dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da Afirka da za a shirya a birnin Beijing, zai samar da wani dandali mai kyau na karfafa hadin kansu a nan gaba, wanda ko shakka babu zai daukaka hadin kan sassan biyu zuwa wani sabon matsayi. (Bilklisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China