Jiya Lahadi shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh, ya bayyana cewa, taron kolin dandalin FOCAC da za a kira a birnin Beijing, zai samar da sabbin damammakin ci gaba ga huldar dake tsakanin Sin da Afirka, haka kuma ga huldar dake tsakanin Sin da Djibouti, kana al'ummun sassan biyu za su kara cin gajiya daga hakan.
Guelleh ya kara da cewa, kasarsa tana son yin kokari tare da kasar Sin, bisa shawarar ziri daya da hanya daya, domin kara karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannoni daban daban.(Jamila)