An dauki kwararan matakan tsaro da na kiwon lafiya don tabbatar da zaman lafiyar mahajjata yayin aikin hajin da za a yi a makon gobe.
Ma'aikatar kiwon lafiyar ta Saudiyya, ta tabbatar da cewa, yanayin kiwon lafiya da kasar take ciki na da kyau. Kuma tuni ta jaddada cewa za ta kara maida hankali kan lafiyar mahajjata, da karfafa hadin-gwiwa da hukumar lafiya ta duniya WHO da sauran wasu hukumomin kiwon lafiya na duniya, domin sa ido da bincike kan yanayin kiwon lafiya da ake ciki da kuma sauye-sauyensa a fadin duniya.(Murtala Zhang)