Kawo yanzu mutane 6 aka ceto, yayin da ake ci gaba da aikin don binciko wadanda suka makale.
Akalla mutane 25 ne ke cikin ginin wanda ake ginawa a unguwar Jabi na Abuja a lokacin da ya rufta jiya da rana.
Mamakon ruwan sama da aka yi a birnin jiya, ya kawo tsaiko ga aikin ceton.
Tuni dai aka fara gudanar da bincike don tantance musababbin rushewar ginin. (Fa'iza Mustapha)