Ma'aikatar harkokin wajen Sudan ta yi tir da wannan hari, tana mai bayyana shi da kazamin laifi, wanda ya keta alfarmar rayuwar bil Adama, da kyawawan dabi'u na mutumtaka. Sanarwar da ma'aikatar ta fitar ta kuma kunshi sakon ta'aziyya ga iyalan jami'in da ya rasu, da kuma fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.
A daya hannun kuma, ta jaddada goyon bayan Sudan ga duk wani mataki na marawa Jordan baya, wajen daukar matakan inganta tsaron kasa, da ba da kariya ga al'ummarta, musamman daga 'yan ta'adda da masu nufin aikata muggan laifuka. (Saminu Hassan)