in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu tsara manufofi na Afirka sun cimma matsaya game da raya bangaren ICT
2018-08-13 20:22:43 cri
A yau ne manyan masu tsara manufofi daga kasashen Afirka suka cimma matsaya guda da nufin raya bangaren sadarwa na zamani tare da sanya shi cikin ajandar raya nahiyar.

Masana da masu tsara manufofi dake ganawa a birnin Nairobin Kasar Kenya gabanin taron kolin kungiyar sadarwa ta duniya da zai gudana a kasar Dubai cikin watan Oktoba, sun bayyana cewa, akwai bukatar cimma matsaya domin hanzarta raya harkokin masana'antun nahiyar ta hanyar amfani da fasahohin kere-kere da kirkire-kirkire.

Babban sakararen fasahar ICT a fadar shugaban kasar Kenya Joe Mucheru ya jaddada cewa, hade manufofi da tsare-tsare sune za su tabbatar da cin gajiyar fasahohin zamani daidai wa daidaida a nahiyar ta Afirka.

Haka kuma, ana fatan idan har aka yi magana da murya guda, kasashen na Afirka za su samu saukin cin gajiyar dake tattare da ci gaban fasahar ta ICT a duniya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China