in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sassan kasar Amurka sun yi suka kan matakin gwamnatin kasar na matsawa sauran kasashe lamba
2018-08-11 18:55:46 cri
A makon da muke ciki, gwamnatin kasar Amurka ta dauki matakai bi da bi don matsawa sauran kasashen duniya lamba, inda ta mayar da takunkumi kan kasar Iran, da hana fitar da wasu fasahohi ga kasar Rasha, gami da kara karbar haraji kan kayayyakin karafa da na saholami na kasar Turkiya. Sai dai matakan da gwamnatin Amurka ta dauka sun janyo suka daga cikin gidan kasar.

Jaridar New York Times ta ruwaito Chad Bown, wani masanin ilimin tattalin arziki dake aiki a cibiyar nazarin tattalin arzikin kasa da kasa ta Peterson, na cewa, matakan da Amurka take dauka wata alama ce da ke janyo damuwa.

A nashi bangaren, Eswar Prasad, wani shehun malami na jami'ar Cornell, ya ce gwamnatin kasar Amurka ta kan dauki matakin da ya shafi harajin kwastam wajen daidaita sabanin ra'ayi a fannin diplomasiyya. A ganinsa, hakan wani mummunan misali ne dake haddasa fargaba.

Ban da haka, Edward Price, wani tsohon jami'i a lokacin gwamnatin Barack Obama, ya ce matakan da kasar Amurka ta dauka na matsawa sauran kasashe lamba ba za su taimakawa daidaita matsalolin da ake fuskantar ba, maimakon haka jama'ar kasar Amurka su ne za su sha wahalar matakan. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China