Lauyansa Nqobizitha Mlilo ya tabbatar da kame Biti, inda ya ce jami'an tsaron sun damke shi ne a yankin Chirundu, dake kan iyakar Zimbabwe da Zambia.
Kame Biti dai ya biyo bayan sanarwar da jami'an tsaro suka fitar a Litinin din da ta gabata, inda suka anya shi, da sauran wasu kusoshin jami'iyyar adawa ta MDC su 8 da hannu, cikin tashin hankalin da ya barke, bayan fidda sakamakon zaben shugaban kasa a birnin Harare, fadar mulkin kasar, lamarin da ya sabbaba kisan mutane 6, tare da raunata wasu da dama. (Saminu Hassan)