in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi kiran da a kai zuciya nesa a Zimbabwe
2018-08-08 10:39:22 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi kira ga sabon zababben shugaban kasar Zimbabwe Emmeson Mnangagwa da abokin hamayyarsa Nelson Chamisa da su kai zuciya nesa, su kuma gabatar da korafe-korafensu ta hanyar da doka ta tanada.

Mataimakin kakakin babban sakataren MDD Farhan Haq, ya shaidawa manema labarai cewa, jiya Talata babban sakataren MDDr ya tattauna ta wayar tarho da shugaba Mnangagwa da kuma jagoran jam'iyyar MDC Nelson Chamisa, inda ya bayyana musu karara cewa, yana fatan shugaban na Zimbabwe zai tabbatar da cewa, jami'an tsaro sun yi taka tsan-tsan. Ya kuma karfafawa bangaren adawa gwiwar da su gabatar da kokensu na siyasa ta hanyar da doka ta shata.

Babban sakataren MDDr ya kara da cewa, ya kamata duk wani hukunci da kotu ta yanke game da sakamakon zabukan ya kasance mai zaman kansa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China