'Yan sandan Zimbabwe sun bayyana hakan ne a Talatar nan, suna masu cewa mutanen da ake nema, suna da ruwa da tsaki wajen kitsa tashin hankalin na birnin Harare, wanda ya biyo bayan bayyana sakamakon babban zaben da shugaban kasar mai ci Emmerson Mnangagwa ya lashe.
Tuni dai aka cafke mutane a kalla 27 bisa wannan lamari, wadanda kuma ake sa ran a Talatar nan za a gurfanar da su gaban kuliya, a wani mataki na neman masu beli. (Saminu Hassan)