in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta sake yin gargadi game da karuwar yanayin zafi
2018-08-05 15:37:08 cri
Hukumar hasashen yanayi ta kasar Sin (NMC) ta sake yin gargadi a yau Lahadi game da karuwar zafi da za'a samu a mafi yawan yankunan kasar.

Tun daga yau Lahadi, mafi yawan yankunan kudancin Yangtze River, Liaoning, Hebei, Shandong, Shaanxi, Sichuan, Guangdong da kuma yankin Xinjiang za'a samu karuwar zafi wanda zai iya kaiwa maki 35-36 a ma'aunin Celsius, in ji hukumar ta NMC.

Wasu yankunan ma yanayin zai karu zuwa maki 39 a ma'aunin Celsius.

Cibiyar hasashen yanayin tana shawaratar jama'ar dake zaune a yankunan da abin ya shafa da su dauki matakan kariya daga matsanancin zafin da kuma wuta, matakan da suka hada da kaucewa wasu harkoki na yau da kullum da za su iya jefa rayuwarsu cikin hadari. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China