Kakakin hukumar 'yan sandan kasar Charity Charamba ya fadawa taron manema labarai cewa, birnin Harare ya kasance cikin mummunan yanayi na tashin hankali kwana guda bayan da rikici ya barke lamarin da ya yi sanadiyyar rayukan jama'a da barnata dukiyoyi.
Magoya bayan jam'iyyar adawa ta MDC sun yi fito na fito da jami'an tsaro a ranar Laraba, a daidai lokacin da suka fara zanga zangar nuna kin amincewa da jinkirin bayyana sakamakon zaben shugaban kasar, hakan ya sa aka tura jami'an sojoji inda suka bude wuta kan masu boren domin tarwatsa su. (Ahmad Fagam)