Kakakin shugaban kasar Femi Adeshina, ya ce shugaba Buhari zai shafe kwanaki 10 yana hutun.
Ya ce shugaban kasar ya mika wasika ga majalisun dokokin kasar, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada. Haka kuma, ya ba mataimakinsa damar rike ragamar shugabancin kasar a madadinsa.
Ko a ranar 8 ga watan Mayun da ya gabata, shugaban ya yi wata gajeriyar tafiya zuwa birnin London domin duba lafiyarsa. (Fa'iza Msutapha)