Aikin hajjin na wannan shekarar wanda za'a gudanar a tsakiyar watan nan na Augasta, an tsaurara matakan tsaro da kuma daukar matakan kare lafiyar mahajjata, in ji hukumar lafiyar.
Ma'aikatar lafiyar kasar mai tsarki tana bibiyar irin ci gaba da kuma sauye sauyen da ake samu game da sha'anin kiwon lafiya na duniya tare da yin hadin gwiwa da hukumar lafiya ta duniya WHO da sauran humumomin kiwon lafiya na kasa da kasa. (Ahmad Fagam)