Buhari ya karbi ragamar jagorancin ECOWAS daga takwaransa na kasar Togo Faure Gnassingbe, biyowa bayan zaben da ya kasance daya daga cikin muhimman kudurorin taron na wannan karo.
Cikin jawabinsa na amincewa, shugaba Buhari ya alkawarta gudanar da ayyuka cikin hadin gwiwa da sauran takwarorinsa, ciki hadda wanzar da tsaro, da zaman lafiya, da mulki na gari, tare da tabbatar da kara raya ci gaban shiyyar yammacin Afirka, da daga matsayin kungiyar ta ECOWAS.
Ana fatan gudanar da taron kungiyar na gaba a ranar 21 ga watan Disambar karshen shekarar nan a Abuja fadar mulkin Najeriya. (Saminu Hassan)