in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren MDD ya yi Allah wadai da harin kunar bakin waken da aka kai a Pakistan
2018-07-26 09:20:15 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi Allah wadai da harin kunar bakin waken da aka kai a ranar zabe a wajen wata tashar kada kuri'a a Quetta, babbar birnin lardin Balochistan dake kudu maso yammacin kasar Pakistan, inda mutane 31 suka rasa rayukansu baya ga wasu 40 kuma da suka jikkata.

Guterres wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa ta hannun kakakinsa Stephane Dujarric, ya kuma aike da sakon ta'aziya ga gwamnati da al'ummar Pakistan da ma iyalan wadanda harin ya rutsa da su. Ya kuma ce MDD tana goyon bayan matakan da mahukuntan Pakistan ke dauka kan yaki da ayyukan ta'addanci.

Koda a tsakiyar watan Yulin wannan shekara ma, mutane 149 ne suka gamu da ajalinsu sakamakon wani harin kunar bakin wake da aka kaddamar yayin gagamin yakin neman zabe a garin Mastung dake lardin na Balochistan. Ana zargin kungiyar IS da kaddamar da hare-haren. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China