Mataimakin shugaban hukumar yayata bayanai ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, gami da sauran wasu manyan jami'ai daga kasashen Afirka ta Kudu da Botswana sun halarci bikin.
A nata bangaren, shugabar karba-karba ta kwamitin kula da harkokin kudi na gamayyar kasashen kudancin Afirka ko kuma SADC a takaice, Nthabiseng Khunou ta yi jawabi, inda ta ce, bikin nunin fina-finan kasar Sin a Afirka, zai kara samar da fahimtar juna tsakanin jama'ar Sin da Afirka, kuma tana maraba da zuwa fina-finan kasar Sin a nahiyar ta Afirka. (Murtala Zhang)