in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mamban majalisar gudanarwar kasar Sin ya gana da Darakta Janar na WHO
2018-07-18 09:58:18 cri
Mamba a majalisar gudanarwar kasar Sin kuma Ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gana da Darakta Janar na hukumar lafiya ta duniya WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus.

Wang Yi ya bayyana lafiya a matsayin jigo ga mu'amalar al'ummar duniya, kuma tushen ci gaban kowacce kasa.

Ya ce a shirye kasar Sin ta ke, ta hada hannu a fannin kiwon lafiya da shirin hukumar WHO na shekaru 5 masu zuwa, karkashin shirinta na "Ziri daya da hanya daya", da kuma tsarin hadin gwiwar kasar Sin da Afrika da kuma burinta na samar da al'umma mai matsakaiciyar ci gaba ta kowacce fuska kamar yadda yake kunshe cikin burika 2 da take son cimmawa yayin da take bikin shekaru 100 guda 2, da nufin taimakawa ci gaban kiwon lafiya a duniya da amfanawa zuri'a na gaba.

A nasa bangaren, Shugaban na WHO, ya bayyana godiyarsa ga taimakon da kasar Sin ke ci gaba da bayarwa ga harkar kiwon lafiya a duniya, da kuma kudurin WHO na shiga cikin shawarar "Ziri daya da Hanya daya". (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China