in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ya tsawaita shirin tsagaita bude wuta a dukkan yankunan dake rikici zuwa karshen shekarar nan
2018-07-13 14:24:05 cri
Shugaban kasar Sudan, Omar al-Bashir, ya bada wata umarnin da ta tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta a yankunan dake rikici har zuwa karshen bana.

Wannan matakin ya biyo bayan dabarar da gwamnati ta dauka na daukaka zaman lafiya da aiwatar da sakamakon taron tattaunawar batutuwan kasa.

Cikin shekarun da suka gabata, Gwamnati da bangaren dake adawa da ita sun ci gaba da sabunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a yankunan dake fama da rikici.

A watan Yunin 2016 ne, shugaba al-Bashir ya fara ayyana tsagaita bude wuta da watanni hudu, domin ba 'yan tawaye damar halartar taron tattauna batutuwan kasa. Tun daga wancan lokaci ne kuma ake ta tsawaita yarjejeniyar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China