in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco da Nijar sun amince su bunkasa hadin gwiwa a fannin muhalli
2018-07-12 09:40:13 cri
A jiya ne a birnin Rabat kasashen Morocco da jamhuriyar Nijar suka sanya hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna da nufin bunkasa hadin gwiwa da tsare-tsare a fannonin canjin yanayi, tsirrai,Ilimin muhalli da ci gaba mai dorewa.

Karamin sakatare mai kula da shirin ci gaba mai dorewa na kasar Morocco Nezha El Oufi da ministan muhalli da raya birane da shirin ci gaba mai dorewa na Jamhuriyar Nijar Almoustapha Garba ne suka sanya hannu kan yarjejeniyar a madadin kasashensu.

Bangarorin biyu sun kuma amince su aiwatar da ayyukan da suka cimma a tsakaninsu, musamman a bangaren hadin gwiwar kasa da kasa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China