in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya ta tusa keyar bakin haurin Nijar 355 zuwa gida
2018-07-12 09:35:10 cri
Hukumar kare hakkin bil-Adam ta kasar Aljeiya ta bayyana cewa, mahukuntan kasar sun tusa keyar bakin haure 355 daga jamhuriyar Nijar zuwa gida.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar a jiya Laraba ta nuna cewa, bakin hauren sun tashi ne daga birnin Algiers zuwa lardin Tamanrasset dake kan iyakar Nijar da kasar Mali. Wata tawagar hukumar mai kunshe da likitoci daban-daban da masana tunanin dan-Adam ne ta yiwa ayarin masu ba da agajin jin kai dake kula da aikin mayar da bakin hauren rakiya.

Sanarwar ta bayyana cewa, kafofin watsa labarai na gida da na ketare sun kalli shirin mayar da bakin hauren zuwa kasashensu na asali, wanda ya kuma samu halartar masu sa–ido daga hukumomin MDD dake kasar Aljeriya, kamar babbar hukumar kula da 'yan gudun hijira da hukumar kula da kaurar jama'a ta duniya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China