in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: An bude wani sabon babi a dangantakar Sin da kasashen Larabawa
2018-07-11 10:22:39 cri
Mamba a majalisar gudarwar kasar Sin kana ministan harkokin wajen kasar ta Sin, Wang Yi, ya ce Sin da kasashen Larabawa sun bude wani sabon babi a dangantakar manyan tsare-tsare da samun ci gaba na bai daya dake tsakaninsu.

Wang wanda ya bayyana hakan yayin da yake shugabantar taron dandalin ministocin Sin da kasashen Larabawa, ya ce Sin da kasashen Larabawa sun kara fadada alakar dake tsakaninsu karkashin shawarar Ziri daya da Hanya daya. Kana kasar Sin tana kokarin bude kofa ga kasashen waje yayin su kuma kasashen Larabawa ke kara zamanatar da masana'antu da fadada tattalin arzikinsu.

Jami'in na kasar Sin ya kara da cewa, muhimman fannoni guda uku da aka amince da su a yayin ganawar, sun hada da sanarwar Beijing, da matakan da za a dauka game da hadin gwiwar Sin da kasashen Larabawa a fannin shawarar ziri daya da hanya daya, da matakan da aka tsara daga shekarar 2018 zuwa 2020 don kara bunkasa wannan dandali, kundin da ya yi bayani dalla-dalla game da yadda za a bunkasa alakar Sin da kasashen Laraba a nan gaba.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China