in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan tsaro: Kasar Sin zata karfafa hadin gwiwar tsaro tsakaninta da kasashen Afrika
2018-07-11 10:07:11 cri
Wakilin majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan tsaron kasar Wei Fenghe ya jaddada aniyar karfafa hadin gwiwa tsakanin Sin da Afrika ta fuskar tsaro da tabbatar da zaman lafiya, ministan ya bayyana hakan ne a jiya Talata yayin ganawa da wakilan kasashen Afrika 49 a taron kolin da aka gudanar a birnin Beijing.

Ya ce nasarorin da aka samu karkashin hadin gwiwar zai taimaka wajen daga matsayin kyakkyawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen Afrika.

Taron dandalin hadin gwiwar tsaron na Sin da Afrika wanda shine irinsa na farko, ya samu halartar wakilan gwamnatin Sin, da kasashen Afrika da kuma kungiyar tarayyar Afrika, wanda aka bude shi tun a ranar 26 ga watan Yuni kana aka kammala taron a jiya Talata.

Wakilan kasashen Afrika da suka halarci taron sun bayyana kyakkyawar fatansu na yin hadin gwiwa tsakanin kasashensu da kasar Sin a aikace daga dukkan fannoni.

A taron dandalin, wakilan sun tattauna tare da cimma matsaya game da batutuwan da suka shafi yadda za'a kyautata makomar rayuwar al'ummomin Sin da kasashen Afrika a nan gaba da kuma karfafa hadin gwiwa Sin da Afrika a fannin aikin soji a sabon zamani. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China