in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in wanzar da zaman lafiya dan Nijeriya ya mutu a Gambia saboda matsalar numfashi
2018-07-06 09:31:14 cri
Rundunar shiga tsakani ta kungiyar ECOWAS dake aiki a Gambia wato ECOMIG, ta sanar da mutuwar jami'inta Abubakar Abdullahi, dan asalin Nijeriya sanadiyyar matsalar numfashi.

Kwamandan rundunar ECOMIG, Colonel Fulgence Ndour, ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar jiya Alhamis cewa, Abubakar Abdullahi soja ne mai mukamin Staff Sergeant a rundunar sojin Nijeriya.

Sanarwar ta ce Marigayin mai shekaru 46, ya rasu ne da sanyin safiyar ranar Laraba. Ta ce an lura da yadda numfashinsa ya samu matsala ne yayin da yake barci, inda aka garzaya da shi asibiti, sai da bai rayu ba.

Rundunar ECOMIG, ta mika ta'aziyyarta ga iyalan marigayin da kuma rundunar sojin Nijeriya bisa wannan rashi.

Rundunar ECOMIG ta isa Gambia ne a watan Disamban 2016, domin tabbatar da muradin al'ummar kasar, bayan tsohon Shugabansu Yahaya Jammeh ya ki amincewa da sakamakon zaben shugaban kasar. Rundunar ta kunshi 'yan asalin kasashen kungiyar ECOWAS ta kasashen yammacin Afrika, ciki har da Senegal da Nijeriya da kuma Ghana. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China