in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta aiwatar da matakin mayar da martani bayan da Amurka ta dauki matakin kara yawan haraji kan kayayyakin Sin
2018-07-05 13:30:29 cri

Babbar hukumar kwastam ta kasar Sin ta bayyana yau Alhamis ranar 5 ga wata, cewar bisa sanarwa mai lamba 5 ta shekarar 2018, wadda kwamitin kula da ka'idojin haraji na majalisar gudanarwar Sin ya fitar, kasar za ta aiwatar da matakin kara karbar yawan haraji kan wasu kayayyakin Amurka da za su shiga cikin kasuwannin Sin, bayan Amurka ta fara daukar matakan kara yawan haraji kan kayayyakin Sin a hukumance.

Wani mai kula da aikin karbar haraji na babbar hukumar kwastam ta Sin ya bayyana hakan, yayin da yake amsa tambayar da kafofin watsa labarai suka yi, game da lokacin daukar matakan mayar da martani kan kara karbar harajin da Amurka za ta yi wa Sin.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China