Fadar shugaban kasa a kasar Cote d'Ivoire, ta bayyana rushe gwamnatin da firaminista Amadou Gon Coulibaly ke jagoranta. Wata sanarwa da babban sakataren fadar gwamnatin Patrick Achi ya fitar, ta ce da wannan sanarwa, wa'adin aikin firaminista Coulibaly ya zo karshe.
Sai dai kuma sanarwar ta sanar da sake nada Mr. Coulibaly a matsayin firaministan sabuwar gwamnatin da za a kafa, shi ne kuma zai jagoranci aiwatar da wannan aiki.
A daya hannun kuma, sanarwar ta ce dukkanin ministocin tsohuwar gwamnatin, za su ci gaba da gudanar da ayyukan ma'aikatunsu, har ya zuwa lokacin da za a rantsar da mambobin sabuwar majalissar zartawar kasar.(Saminu)