MDD ta yi kiyasin yara miliyan 2 da dubu 200 da suka cancanci shiga makaranta a Sudan ta kudu ne ba su yin karatun sakamakon matsalolin tashin hankali da durkushewar tattalin arziki da kasar ta gabashin Afrika ta fada cikinsa.
Sardar Umar Alam, jami'in sashen ilmi na MDD, kana wakilin hukumar raya ilmi da kimiyya da al'adu ta MDD (UNESCO) dake kasar, ya ce samun 'yancin kasar bai amfanawa kananan yaran kasar da komai ba sakamakon yakin basasar da kasar ta tsunduma da yaki ci yaki cinyewa.(Ahmad Fagam)