Kasar Sin za ta ci gaba da goyon-bayan kyautata alaka tsakanin Koriya ta Arewa da ta Kudu
Yau Litinin, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lu Kang ya bayyana cewa, kasarsa za ta ci gaba da nuna cikakken goyon-baya ga daidaita dangantaka tsakanin Koriya ta Arewa da ta Kudu, tana kuma fatan kasashen duniya za su kara ba su kwarin-gwiwa.
Rahotanni na cewa, a kwanakin nan, Koriya ta Arewa da ta Kudu na ci gaba da yin mu'amala da juna. Game da haka, Lu Kang ya ce, kasar Sin na matukar farin-cikin ganin cewa, bangarorin biyu na kara tuntubar juna da cimma matsaya daya kan karin fannoni.(Murtala Zhang)