Sojojin kasar Sin sun gina wata cibiyar hana yaduwar cututtuka a Saliyo
Kakakin ma'aikatar tsaron kasar Sin Wu Qian, ya furta a yau Alhamis cewa, sojojin kasar Sin sun kusa kammala gina wata cibiyar hana yaduwar cututtuka a kasar Saliyo. Cibiyar da za ta kasance irinta ta farko da sojojin Sin suka gina, a matsayin wani tallafi ga nahiyar Afirka. Za a shirya bikin mika cibiyar a farkon watan Yuli dake tafe. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku