Wannan jami'i ya bayyana cewa, dakaru sun kai hari ga kauyuka 11 dake jihar Plateau a daren ranar 23 ga wata. A halin yanzu, yawan mutane da suka mutu a sakamakon harin ya haura 200, kuma adadin zai iya ci gaba da karuwa.
Bisa labarin da aka bayar, an ce, a cikin kauyuka 11 da aka kaiwa harin, yawan mutanen da suka mutu a kauyen Ruku ya zarce 47. Banda salwantar rayuka da raunatar mutane, harin ya kuma lalata wasu gine-gine da motoci. (Zainab)