in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren MDD ya yi kiran ga kasashen duniya da su hada hannu don hana fataucin miyagun kwayoyi
2018-06-27 11:39:21 cri
Babban sakataren MDD Antoni Guterres ya yi kira ga kasashen duniya da su hada hannun tare da bullo da maganartan dokoki don hana aikata munanan laifuffuka da ma fataucin miyagun kwayoyi.

Cikin sakon da ya aike albarkacin ranar yaki da sha da safarar miyagun kwayoyi ta duniya da aka yi bikinta a jiya Talata, babban sakataren MDDr ya ce kalubalen miyagun kwayoyi na daga cikin matsaloli masu sarkakiya da duniya ke fuskanta a halin yanzu, lamarin dake yin mummunan tasiri ga lafiyar bil-Adama, iyalai, al'ummomi da tsaro da samun ci gaba mai dorewa.

Ya ce, muddin ana bukatar magance wadannan matsaloli, wajibi ne a dauki matakai daban-daban, kamar yadda ya ke kunshi cikin sakamakon muhimman bayanan da babban taron MDD na musamman da ya gudana a shekarar 2016 game da matsalar miyagun kwayoyi a duniya ya amince da shi bai daya

Jami'in na MDD ya ce, baya ga hadin gwiwar kasa da kasa da amfani da managartan dokoki, akwai bukatar a fafada matakai na zahiri kan yadda za a kare, a magance, a kuma bada taimako don a kawo karshen wannan matsala.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China