Sudan ta yi tir da harin da aka kai kan gangamin siyasa a garin Bulawayo na Zimbabwe, tana mai bayyana shi a matsayin laifin take darajar dan Adam da 'yan uwantaka a tsakanin al'ummar Afrika.
Wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen Sudan ta fitar, ta kuma jajantawa gwamnati da al'ummar Zimbabwe tare da yi wa wadanda suka raunana fatan samun sauki cikin gaggawa.
Ma'aikatar ta kuma jadadda matsayin Sudan na adawa da duk wani nau'i na laifuka da hari kan mutanen da ba-su-ji-ba-ba-su-gani-ba.
A ranar Asabar da ta gabata ne shugaban Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, ya tsallake rijiya da baya, biyo bayan wani hari da aka kai kan gangamin siysasa, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 2 tare da raunata wasu da dama. (Fa'iza Mustapha)