in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar MDD mai kula da 'yan ci ranin Falasdinu na neman tallafin dala miliyan 250
2018-06-26 11:02:19 cri
Hukumar MDD dake kula da Falasdinawa 'yan gudun hijira, na neman tallafin kusan dala miliyan 250, don cike gibin kudin da take bukata a bana.

Da yake ganawa da manema labarai kafin wani taron neman tallafi da ya gudana jiya, wanda kwamitin wucin gadi na babban zauren MDD ya shirya, shugaban hukumar Pierre Krahenbuhl ya nemi kasashe mambobin majalisar su ba da tallafi mai yawa.

Hukumar UNRWA a takaice, ta shiga wannan shekarar ne da gibin dala miliyan 146.

Yanayin da take ciki ya kara tabarbarewa ne bayan gwamnatin Amurka ta zaftare dala miliyan 300 daga cikin tallafin da take ba hukumar. Amurka ta kasance kasa mafi tallafawa hukumar cikin gomman shekaru da suka gabata. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China