in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da taron manyan jami'an kasar Sin da kungiyar EU ta fuskar tattalin arziki da cinikayya a Beijing
2018-06-25 21:12:12 cri
A yau Litinin, an gudanar da taron manyan jami'an kasar Sin da na kungiyar EU ta bangaren tattalin arziki da cinikayya karo na 7 a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Taron wani tsari ne na musayar ra'ayi a matsayin koli, wanda ya kasance tsakanin Sin da nahiyar Turai, dake gudana a wannan karo karkashin jagorancin mataimakin firaministan kasar Sin Liu He, da mataimakin shugaban kwamtin kungiyar EU Jyrki Kataine.

Taron da aka yi a wannan karo na tare da dimbin sakamako, wadanda da farko suka shafi ra'ayi daya da Sin da kungiyar EU suka cimma, na yaki da daukar ra'ayin kashin kai, da kuma manufar kariyar ciniki. Inda bangarorin 2 suka yi alkawarin kare tsarin ciniki mai mutunta kungiyar ciniki ta duniya WTO, gami da ka'idojin kasa da kasa, ta yadda za a samu damar kyautata tsarin tattalin arzikin duniya.

Sauran nasarorin da aka samu a wajen taron sun shafi yadda za a hada shawarar "Ziri Daya da Hanya Daya" ta kasar Sin da tsarin raya tattalin arziki na nahiyar Turai, da hadin gwiwar bangarorin 2 a fannonin tinkarar sauyawar yanayin duniya, da hada-hadar kudi, aikin gona, da dai makamantansu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China