in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan wasan gaba na Nijeriya ya sha alwashin cin kwallo a wasan da za su kara da Argentina
2018-06-23 16:41:35 cri
Ahmed Musa, dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafar Nijeriya, wanda ya ci kwallaye biyun da suka taimkawa kasar doke Iceland da ci 2 da nema, ya ce zai ci gaba da kyautata fata tare da alkawarin kara cin kwallo a wasan karshe na rukunin D da za su buga da Argentina, a gasar cin kofin duniya dake gudana a Rasha.

Ahmed Musa ya ce yana ganin cin Argentina ba abu ne mai wahala ba, inda ya ce suna sane cewa wasan da za su buga da Argentina na da muhimmanci, yana mai bayyana ta a matsayin na ko a mutu-ko-a-yi-rai.

Croatia ta samu maki 6 daga nasarori biyu da ta samu, inda za ta jagoranci rukunin, kuma idan Nijeriya ta samu damar doke Argentina, to za ta shiga jerin kasashe 16 da za su buga zagaye na 2 na gasar tare da Croatia, inda za su kora Argentina gida.

Dan wasan ya ce zai iya tunawa shekaru 4 da suka gabata, ya ci kwallaye 2 yayin da suke wasa da Argentina. Kuma da ya bugawa Leicester wasa a shekarar 2016, ya buga wasan sada zumunta da Barcelona inda Messi ke buga kwallo, kuma a nan ma ya zura kwallaye 2.

A don haka, ya ce a ganinsa, komai zai iya faruwa a wasa na gaba. Ya kara da cewa, abu mai yuwuwa ne ya kara shan wasu kwallayen 2. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China