in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana fatan za a warware batun zirin Koriya a siyasance
2018-06-19 19:49:50 cri

Yau Talata ma'aikatar tsaron kasar Koriya ta Kudu da ta Amurka sun fitar da wata sanarwar hadin gwiwa, inda suka bayyana cewa, kasashen biyu sun tsai da kudurin dakatar da atisayen aikin soja wato UFG, wanda aka tsara gudanarwa a watan Agusta mai zuwa, domin tabbatar da wannan buri na raba zirin Koriya da makaman kare dangi, da kuma kafa tsarin shimfida zaman lafiya a zirin.

A dai wannan rana, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya nuna maraba da wannan mataki, inda ya bayyana a yayin taron ganawa da manema labaran da aka saba yi cewa, ana fatan sassan biyu za su ci gaba sanya kokari, domin samun sabon ci gaba a fannin.(Jamila)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China