in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Iraqi ta musanta cewa rundunar kawance da Amurka ke jagoranta ta yi luguden wuta kan jami'anta dake iyakar kasar da Syria
2018-06-19 11:32:58 cri
Rundunar sojin Iraqi, ta musanta cewa luguden wuta ta sama ya rutsa da jami'anta dake aiki a kusa da iyakar kasar da Syria.

Rundunar tsaron hadin gwiwa ta Iraqi, ta ce dukkan jami'an tsaro da suka hada da sojoji da 'yan sanda na Hashd Shaabi na tsare da iyakokin kasar, ciki har da wadanda ke kan iyakar Iraqi da Syria, kuma babu wani luguden wuta ta sama ko wani hari da ya auka musu.

Sanarwar ta kuma tabbatar da cewa an kai harin ne kan hedkwatar tsaro dake yankin al-Hiri dake yankin kudancin al-Bukamal na gabashin Syria, wanda ke da lambuna da gidaje dake da nisan kilomita 1.5 daga iyakar Iraqi da Syria.

Da farko a ranar, rundunar Hasd Shaab ta fitar da wata sanarwa, inda ta ce 22 daga cikin mambobinta sun mutu, wasu 12 kuma sun jikkata, sanadiyyar wani hari da take zargin rundunar kawance da Amurka ke jagoranta ta kai sansaninta dake cikin Syria, wanda ke kusa da iyakar Iraqi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China