An bude taron kasa da kasa kan fasahar noman ciyayi karo na 16 a lardin Fujian na kasar Sin, taron wanda ya samu halartar wakilai daga kasashen duniya da shiyoyi sama da 30 ciki har da wakilai da kwararrun masana daga nahiyar Afrika, kana akwai kuma dalibai daga jami'oin kasar Sin dake nazartar fannin noman ciyaye kamar lemar kwadi da dai sauransu. Abokin aikinmu Ibrahim Yaya wanda ya samu halartar taron yayi mana karin haske dangane da makasudin shirya wannan taro, ga abinda yake cewa: