in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya bukaci a yi kokarin bunkasa kirkire-kirkire don raya tattalin arziki da zamantakewa
2018-06-15 11:11:25 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a kara kokarin aiwatar da sabon burin ci gaba, domin samun ci gaba mai inganci, tare da bunkasa kirkire-kirkire domin raya tattalin arziki da zaman takewa da kuma gamsar da bukatun al'umma dake karuwa, da nufin kyautata rayuwarsu.

Xi Jinping, wanda shi ne shugaban kwamitin tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kwamitin sojan kasar, ya yi wannan jawabi ne yayin da yake rangadi a lardin Shandong na gabashin kasar, daga ranekun 12 zuwa 14 ga wata.

Shugaba Xi ya kuma yi kira da a yi kokarin daukaka darajar masana'antu da kirkire-kirkiren dake inganta ci gaba da inganta kayakin more rayuwa da mayar da Shandong muhimmin lardi da ake zirga-zirgar jiragen ruwa da inganta bude kofa da sauye-sauye, da kuma samun nasara wajen cimma ci gaba mai inganci.

A matsayinsa na babban lardin a fannin aikin gona, shugaba Xi ya ce hakkin Shandong ne, tabbatar da wadatar abinci a kasar, yana mai kira da a kara kokarin samar da kayakin abinci da inganta aikin gona da kara kudin shigar manoma da yaki da talauci da aiwatar da tsarin zamanantar da aikin gona da yankunan karkara da kuma mayar da Shandogon lardin misali na aiwatar da wannan tsari. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China