in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da taron ministocin CASCF na 8 a birnin Beijing
2018-06-14 19:52:55 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Geng Shuang, ya ce ministocin kasashe mambobin dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Labarawa, za su gudanar da taron dandalin karo na 8 a nan birnin Beijing. An dai shirya gudanar da taron ne na dandalin CASCF a ranar 10 ga watan Yuli mai zuwa.

Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, da ministoci, da wakilan kasashen Labarabawa, da kuma babban sakataren kungiyar kasashen Larabawa ta LA, na cikin wadanda ake fatan za su halarci taron.

Geng Shuang ya kara da cewa, yayin taron, za a gudanar da tattaunawa mai zurfi, game da zurfafa kawance na gargajiya dake tsakanin sassan biyu, da fadada shawarar nan ta ziri daya da hanya daya. Sai kuma batun bunkasa sabon salon kawance na kasa da kasa, da samar da al'umma mai cin gajiyar makoma ta bai daya.

Har ila yau, za a yi amfani da taron wajen dada karfafa hadin gwiwar Sin da kasashen Larabawa karkashin dandalin na CASCF, da ma sauran batutuwa da suka shafi kasa da kasa, da na shiyya shiyya da ke jawo hankulan sassan biyu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China