in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mike Pompeo zai ziyarci Sin tare da tattauna batun ganawar shugabannin Amurka da koriya ta arewa
2018-06-13 20:18:58 cri
Sakataren wajen Amurka Mike Pompeo, zai kawo ziyara nan kasar Sin a ranar Alhamis, domin gabatarwa Sin din sakamakon ganawar shugaba Donald Trump na Amurka, da takwaransa na koriya ta arewa Kim Jong Un wadda ta gudana a Singapore.

A cewar kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, Mr. Pompeo zai gudanar da ziyarar ne bisa gayyatar da babban dan majalissar zartaswar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya yi masa.

Geng Shuang ya kara da cewa, sassan biyu za kuma su yi musayar ra'ayi, game da dangantakar dake tsakanin kasashen su, tare da muhimman batutuwan da suka shafi kasa da kasa, dana shiyya shiyya, wadanda suke jan hankalin sassan biyu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China