in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar harkokin wajen Sin ta fitar da sanarwa game da ganawar shugabannin Koriya ta Arewa da Amurka
2018-06-12 20:37:24 cri
Yau Talata, ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta fitar da wata sanarwa, dangane da ganawar da aka yi tsakanin shugabannin kaashen Koriya ta Arewa da na Amurka a kasar Singapore, inda ta ce, ganawar ta yi armashi, har ma ta haifar da sakamako mai kyau, al'amarin da ya kasance babban ci gaban da aka samu ta fannin kokarin kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya, da warware matsalar zirin ta hanyar siyasa.

Kaza lika sanarwar ta bayyana cewa kasar Sin ta jinjinawa shawarar da shugabannin kasashen biyu suka yanke, tare da maraba, da goyon-baya ga sakamakon da aka samu a yayin shawarwarin na su. Har ila yau kuma, ta yabawa matukar kokarin da bangarori daban-daban suka yi game da shirya shawarwarin cikin nasara. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China