in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Koriya ta arewa da Amurka sun amince da raba yankin zirin koriya da makaman nukiliya
2018-06-12 19:22:27 cri
Shugaban Koriya ta arewa Kim Jong Un da shugaban Amurka Donald Trump, sun cimma matsaya game da aiwatar da manufar raba zirin koriya da makaman nukiliya, tare kuma da tabbatar da samar da tsaro a yankin.

Shugaba Kim da Mr. Trump sun rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa bayan taron su na yau Talata, a zaman da ya wakana a otal din Capella dake tsibirin Sentosa na kasar Singapore.

Cikin sanarwar hadin gwiwa da suka fitar, shugaba Trump ya ce zai tabbatar da samar da cikakken tsaro ga Koriya ta arewa, yayin da shi kuma shugaba Kim ya nanata aniyarsa, game da kammala dukkanin manufofi da suka shafi raba zirin koriya da makaman nukiliya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China