in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Karin yara 'yan gudun hijira ne aka mayar Niger, yayin da nahiyar Turai da yankin arewacin Afrika ke tsaura tsaron iyakokinsu
2018-06-09 15:42:28 cri
Asusun kula da kananan yara na MDD UNICEF, ya ce karin adadin yara 'yan gudun hijira ne aka mayar Niger, a daidai lokacin da kasashe a fadin nahiyar Turai da yankin arewacin Afrika ke kokarin magance matsalar kaura ba bisa ka'ida ba.

A cewar UNICEF, babu isassun matakan kula da zirga-zirga tsakanin iyakoki dake kare yara daga hadarun da za su iya fuskanta, da suka hada da safararsu da azabtarwa da cin zarafi da kuma tsarewa.

A cewar kakakin hukumar UNICEF kan batun kaura Sarah Crowe, suna ganin yadda ake kara tsaurara matakan tasa keyar 'yan gudun hijira daga Turai da arewacin Afrika.

Tun daga watan Nuwamban bara, sama da 'yan yammancin Afrika 8,000 ciki har da yara 2,000 ne suka koma Niger daga Algeria, yayin da aka mayar da wasu 'yan gudun hijira da masu neman mafaka 900 dake da rejista 'yan asalin kasashen gabashin Afrika, zuwa Niger daga Libya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China